Humumar tsaro ta DSS ta saki wasu mutane uku Fulani da ta kama yayin da suke sauka acikin jirgi bayan sun dawo daga aikin Hajji a watan yunin 2024
DSS ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a hedikwatar ta dake Abuja inda ta ce ta kama mutanen ne bisa zargin su da hannun su a ayyyukan garkuwa da mutane a arewacin kasar nan
Wadanda hukumar ta kama sun hadar da Rabi’u Alhaji Bello da umar Ibrahim da Bammo Jajo Sarki dukan su yan jihar kwara
Hukumar ta DSS ta ce ta kammala bincike a kan su kuma bata same su da laifin komai ba hakan ce ta sa ta baiwa kowannen su kyautar naira miliyan daya
Kungiyoyin Fulani sun sha kokawa kan kama mutanensu game da zargin garkuwa da mutane da kuma ta’adanci ba tare da wata hujja ba inda sukace hakan abin takaici ne








