Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun bayyana cewa ƙasar Saudiyya ta aiwatar da hukuncin kisa kan mutane aƙalla 347 a shekarar 2025, wanda ya zarce adadin da aka yi a shekarar 2024.
A cewar rahoton da gamayyar ƙungiyoyin suka fitar a karshen mako, mafi yawan waɗanda aka zartar wa hukuncin kisan sun kasance masu safarar miyagun ƙwayoyi, inda fiye da rabin su ƴan ƙasashen waje ne.
Rahotonnin sun kuma bayyana cewa, daga cikin fursunonin da aka zartarwa hukuncin kisan a bayakwanan nan, akwai ’yan asalin Pakistan masu laifin safarar miyagun ƙwayoyi, wani ɗan jarida, wasu matasa da suka aikata laifi tun suna ƙanana, da kuma mata biyar.








