Hukumar tsaro ta DSS shiyyar Kano, ta ceto wani ƙaramin yaro mai shekaru biyar Muhammad Haruna, wanda aka sace shi a kauyen Dan Zaki da ke yankin ƙaramar hukumar Minjibir.
Sanarwa da hukumar ta DSS ta fitar yau Juma’a ta bayyana cewa, sun ceto yaron ne da misalin karfe 7:40 na yammacin ranar 12 ga watan nan da muke ciki na Fabarairu ta hannun tawagar ta musamman a kauyen Dan Zaki.
Rahoton ya nuna cewa sacewar ta biyo bayan korafin da ya bayyana cewa wasu da ake zargi sun tafi da yaron zuwa wani wuri da ba a sani ba tare da neman kudin fansa Naira miliyan 15.
A yayin aikin, jami’an DSS sun kama wani matashi mai shekara 20, Aminu Mukhtar, yayin da ya ke tattaunawa da mahaifin yaron kan kudin fansa ta lambar waya 07084228695.
Cikin bayanin da aka naɗa daga gare shi, Mukhtar ya amsa cewa ya sace yaron ne domin karbar kudin fansa.
Yanzu haka wanda ake zargi da yaron da aka ceto suna hannun DSS domin ci gaba da daukar matakan da suka dace.
Solacebase








